Wani Bufulatani Ne Ya Kai Matarsa
Asibiti, Lokacin Sallar Magrib Yayi, Sai
Bufulatani Ya Tafi Yayi Sallah, Kafin
Yadawo Sai Aka dauke Wuta
Sai Likita Yabi Gado Gado Yana Raba
Kandir Damin Su kunna,
Bufulatani Ya Dawo Yaga Gadon Kowa
Da Wuta Shi Kuma Gadon Matarsa Ba
Wuta
Sai Yaje Wajen Likita Yace: Naga Ko Ina
Da Wuta Amma Gadon Matata Babu,
Sai Likita Yace Akwae Na Bewa Kowa
Kadir Din, Kaje Ka Tambayi Matarka
Mai Yasa Bata Kunna Ba,
Yana zuwa Yacewa Matarsa Ina Abunda
Likita Yakawo Sai Tace
Maigida Rogon Birni? Ai Nima Dakyar
Na Cinye, Kuma Abunda Yasa Ban Ajiye
Maka Ba, Dan Nasan Ba zaka Iya Ciba,
Dan Nima # Dakyar Nacinye
THE END
POST BY: husna
HAJIYA ME CIN CIN
Wata mata ce tana yin cincin na siyarwa
amma kullum idan ta tashi sai ta ga babu
wani cigaba, ma'ana babu riba ko kadan.
Sai ta yanke shawara ta zauna cikin dare
ko bera ne yake yi ma ta barna ko zata
kama shi. Haka akai kuwa cikin dare
kawai sai ta ji ana ta kurmus-kurmus,
cikin sauri ta haska fitila kawai sai ta ga
mijinta ne yake ta faman tauna, sunahada
ido da shi, sai yace: "Na ci na Hamsin"
THE END
POST BY: gluex
DUK BUHARIYYA CE SO KAKEYI MUYI FADA
Wani magidanci ne yana hira da matarsa sai
yacemata:
Honey gaskiya budurwata Aisha tana qaunata
sosai. Matar tace masa, Gaskiya Aisha
budurwarka ta burgeni.
Maigidan nata yace, Rannan fa har cemin tayi
honey na yadace muje Wellcare domin muyi
siyayyar kayayyaki. Sai matar tace gaskiya ta
burgeni.
Sai mai Gidan nata yace, Jiya fa har cemin
tayi honey I love u very very much. Sai matar
tace masa, Gaskiya budurwarka tana sonka.
Sai mai Gidan yace dazu kuwa tacemun, Ina
my son (danki)? Kinsan tafiki Qaunarsa. Sai
matar tace gaskiya ta burgeni.
Qarshe dai sai mai gidan yacemata, Wai ke
Sadiya babu abinda yake bata miki rai ne?
Budar bakin matar sai tace, Eh babu abinda
zance, ai na ganeka:
Duk BUHARIYYA ce, So kakeyi muyi fada ka
korani gida, Ba inda zani
THE END
POST BY: husna
DAN FULANI JIBRILU A MAKARANTAR KWANA………..HAHAHAHA
Wani yaro ne sunansa jibrilu, aka kai shi
makarantar kwana, a gadon dakin kwanan
dalibai da ke makarantar da aka kai shi hawa
uku ne,
sai aka ba shi gado hawa na uku, cikin dare
fitsari ya kama shi ya rasa yadda zai yi sai ya
fara ihu yana kuka,
sai shugaban daliban wannan dakin ya ce
waye ya ke mana kuka sai yaron ya ce,
Jibrilune daga sama ta uku, gaba daya daliban
da ke dakin kwanan suka fara gudu.
THE END
POST BY: husna
NA MANTA TAKALMINA
Wani Bafulatani ne kullum sai an yi masa sata
a gonarsa. Abu fa ya dami Bafulatani, sai wata
rana ya ce bari na buya ko zan kama
barawon.
Can kawai sai ga barawo ya zo ya debi
amfanin gona ya saba a kafada zai tafi. Sai
Bafillace ya kama shi ya ce “Yau dubunka ya
shika. Lalle yau akoi lugude a rugga.”
Ya tusa keyar barawo suka nufi ruga. Suna
cikin tafiya sai barawon ya ce ya manta
takalminsa a gona, a saboda haka sai dai su
koma su dauko.
Sai dan fulani ya ce “Shabbijan, sai da muka jo
nan sannan za ka she mu koma gona???” Ya
ci gaba da cewa “Ni ba zan koma ba, sai dai
ka yi gudu ka je ka dauko ina jiranka”
Barawo ya yunkara zai sauke kayan sati don
ya koma gona, sai Dan fillo ya ce ” Kai wa ka
ke nufin zai maka gadin kayan satarka?? Ai da
su za ka je ka dawo, ina jiranka, Wallahi kuma
kar ka zauna wasa”
Shiru, shiru barawo bai dawo ba, sai Dan fulani
ya tafi gida, ya je yana bawa baffansa labari,
sai Baffan nasa ya ce, “Amma kai akwai
sakarai, maimakon ka she ya tsaya ka je
kadauko masa.”