Wata Budurwace Ta Ari Wayar Saurayinta
Tana Game Sai Ta Kamo Wurin Da Ake Aje
Sunaye Wato CONTACT tana cikin dubawa
tana cin dariya saboda wasu sunaye da ta
gani ma abin dariya irin su
Khadija mai katon lebo,
Aisha mai goshin jirgi,
Fati mai faso a kafa,
Sadiya mai mai warin baki sai takira wayar shi
da wayarta kwatsan sai taga sunanta kamar
haka
SAFIYA MAI ZARNIN FITSARI.
THE END
POST BY: husna
HAPPY BIRTHDAY BARAWO – INJI BASAKKWACE
Wadansu ’yan fashi ne suka tare mota cike da
fasinja suka sa kowa ya kwanta a kan titi.
Babban barayin ya ci ado, yana zaune.
Sai ya ce yau ba wata sata mai yawa za mu
yi ba saboda yau ce ranar haihuwata.
Kuma sunana Dauda don haka ko mace ko
namiji duk wanda sunansa ya fara da harafin
‘da’ sai ya zo ya fada min sannan ya ce min
“Happy Birthday!” Wani Basakkwace na zuwa
ya ce sunana Duna. “Happy Birthday barawo!”
THE END
POST BY: husna
MUNA SAYA MISHI (MUNTSAYA MATA)
Wani Inyamiri ne ya halarci zaman kotu sai
kuwa ya yi sa’a a ranar ana zaman sauraron
karar wata mace da aikata zamba.
Da aka kammala sauraron karar sai Alkali ya
yanke wa matar hukunci daurin shekaru biyar
ko kuma tarar Naira dubu dari biyu da hamsin.
Sai Alkali ya yi tambaya da cewa za a tafi da
matar gidan kaso amma idan har da akwai
wanda zai tsaya mata, to fa za ta iya samun
‘yancinta.
Inyamiri ya dubu ya ga babu wanda ya mike
ya ce zai tsaya wa matar nan, Sai ya ce a
ransa “Hausa mugu ne walayi, zai bari
wannan mutum ya yi cekala biyaru a prison
saboda tsayawa”
Sai ya mike tsaye ya ce “Alkali, Mun saya
mishi”
Sai Alkali ya ce to tunda an samu wanda zai
tsaya mata ba za a kaita gidan kaso ba. Kai
kuma ya ya sunanka? Alkali ya tambayi
Inyamiri.
Inyamiri ya masa da sunanmu ne Chinedu.
Sai Alkali ya ce to, za ka biya tarar Naira dubu
dari biyu da hamsin don wannan baiwar Allah
ta samu ‘yancinta kamar yadda ka fada cewa
ka tsaya mata.
Chinedu ya ce “Mene ne?”
Alkali ya ce Naira dubu dari biyu da hamsin
Chinedu ya ce ” Na two hundred and fifty
thousand naira be that oo”
Alkali ya kwarai
Sai Chinedu ya ce “Oga Alkali, mun zauna
mishi…kai munkwanta mishi”
THE END
POST BY: husna
WANI MUTUM DA MAHAUKACI
Wanimutum ne yana cikin tafiya, toh dama
akwai wani mahaukaci a gabansa sai
mahaukacin ya ci karo da naira N1000 sai
yayi maza ya dauke.
Sai mutumen nan ya ce masa:- “Kai Mallam
Bani (ID Card) dina sai mahaukacin
Sai mahaukacin ya ce: “hehehe Haba dan Uwa
in ni Mahaukacine Ai ni ba Wawa Bane.”
Toh idan ID CARD din ka ne Menene Sunanka?
Sai mutumin ya ce:-“CENTRAL BANK OF
NIGERIA ”
Sai mahaukacin ya ce:- “Toh Shekarunka fa?”
Sai mutumin ya ce:-‘ “1000” ne.
Sai mahaukacin ya ce:-“Lallai Mallam ID CARD
dinka ne Amshi,amma ka tabbatar kasa hoton
ka nan gaba”
THE END
POST BY: husna
KWADO KO MABUDI?
Wani Bafulatani ne ya je kasuwa wajen da
ake sayar da kwadon rufe kofa. Bayan ya
yi cinikin kwado daya sai aka miko masa
tare da ’yan mabudansa. Bayan ya amsa
sai ya cire ’ya’yan mabudan ya sanya
aljihu, ya mika wa mutimin kwadon, ya ce:
“Ya’yan kawai nake son saye, domin
kasuwar da ta wuce na sayi kwadon,
’ya’yansa ne suka fadi, shi ne na ce bari
in zo in sayi wasu.”